HomeSashen HausaDikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

Dikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

-

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da naɗin sabbin manyan sakatarorin jihar.

 

Gwamnan ya ce an gudanar da naɗin bi sa cancanta da sabbin manyan sakatarorin da aka naɗa suka nuna ta hanyar cin jarabawar da Cibiyar Ma’aikata ta Najeriya ta gudanar a madadin gwamnatin jihar Katsina.

 

Gwamnan wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan jihar Mallam Falalu Bawale, ya buƙaci waɗanda aka naɗan da su yi aiki da ƙwarewa tare da nuna ƙwazo.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, sabbin manyan sakatarorin sun haɗa da Tukur Hassan Dan Ali, Junaidu Muntari da Yahaya Abdullahi.

 

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai na shugaban ma’aikatan jihar Abubakar Yaro Bindawa ya fitar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular