HomeSashen HausaJami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu–...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

-

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da suka aikata.

 

An kama jami’an sojoji 16, ciki har da birgediya janar da kanar, a watan Oktoban 2025. Daga bisani, Hedikwatar Tsaro ta tabbatar da cewa, an gano shirin kifar da Shugaba Bola Tinubu, wanda aka ce an gano shi ne ta hanyar haɗin gwiwar bayanan sirri daga sojoji, DSS da DIA.

 

Da yake magana a wata hira da ya yi da TRT World, Musa ya tabbatar da cewa, za a yi wa waɗanda ake zargi shari’a cikin adalci, tare da ba su damar ɗaukar lauya.

 

Haka kuma, ya ce gwamnati za ta kula da iyalan jami’an da ake zargi.

 

Musa ya jaddada cewa masu hannu a yunkurin sun riga sun san illar abin da suka aikata, kuma suna shirye su fuskanci hukuncin da doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

‘Yanbindiga Sun Ƙone Coci da Ofishin ‘Yansanda, Sun Sace Mutane a Jihar Neja

Rahotanni da ke shigowa daga Jihar Neja na nuni da cewa wasu yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai wani mummunan hari a wani...

Most Popular