HomeSashen HausaSojojin Saman Najeriya Sun Hallaka 'Yanbindiga 27 a Katsina

Sojojin Saman Najeriya Sun Hallaka ‘Yanbindiga 27 a Katsina

-

Rundunar sojojin sama ta Najeriya (NAF), a karkashin rundunar FANSAN YANMA, ta samu babban nasara a jihar Katsina bayan kai farmaki na sama da ya hallaka wasu ‘yan bindiga a ƙaramar hukumar Faskari

 

Zagazola ya samu labarin cewa an gudanar da farmakin ne a safiyar 1 ga watan Fabrairu, inda aka kai hari kan sansanonin da ake zargin ‘yan bindiga suna taruwa a dajin Shawu–Mununu Ruwan Godiya a yankin faskari.

 

Majiyoyi sun ce farmakin ya biyo bayan dogon bincike na sama da ya tabbatar da kasancewar ‘yanbindiga masu makamai a yankin Bakori–Guga, waɗanda ake zargi da kai hare-hare kwanan nan.

 

An yi kira ga al’umma da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga hukumomi domin taimaka musu wajen gano motsin ‘yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Musulman Najeriya 89,000 Ne Suka Yi Umrah a 2025– Inji Saudiyya

Hukumomin ƙasar Saudiyya sun bayyana cewa kusan Musulman Najeriya 89,000 ne suka gudanar da aikin ibadar Umrah a shekarar 2025, inda kashi 92 cikin 100...

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Most Popular