HomeLabaraiSojojin Saman Najeriya Sun Hallaka 'Yanbindiga 27 a Katsina

Sojojin Saman Najeriya Sun Hallaka ‘Yanbindiga 27 a Katsina

-

Rundunar sojojin sama ta Najeriya (NAF), a karkashin rundunar FANSAN YANMA, ta samu babban nasara a jihar Katsina bayan kai farmaki na sama da ya hallaka wasu ‘yan bindiga a ƙaramar hukumar Faskari

 

Zagazola ya samu labarin cewa an gudanar da farmakin ne a safiyar 1 ga watan Fabrairu, inda aka kai hari kan sansanonin da ake zargin ‘yan bindiga suna taruwa a dajin Shawu–Mununu Ruwan Godiya a yankin faskari.

 

Majiyoyi sun ce farmakin ya biyo bayan dogon bincike na sama da ya tabbatar da kasancewar ‘yanbindiga masu makamai a yankin Bakori–Guga, waɗanda ake zargi da kai hare-hare kwanan nan.

 

An yi kira ga al’umma da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga hukumomi domin taimaka musu wajen gano motsin ‘yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

ADC Ta Zargi Tinubu Da Raba Kan ‘Yan Adawa Ta Hanyar NDC

Jam’iyyar ADC ta yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC na da hannu wajen ƙirƙirar sabuwar jam’iyyar NDC domin raunata haɗin...

Vinicius Jr Accused of Reporting Teammates to Madrid Chiefs

Vinicius Jr Accused of Reporting Teammates’ Issues to Real Madrid Chiefs. Reports from several European media outlets claim that Vinícius Júnior is being accused of informing...

Most Popular