HomeSashen HausaSojojin Saman Najeriya Sun Hallaka 'Yanbindiga 27 a Katsina

Sojojin Saman Najeriya Sun Hallaka ‘Yanbindiga 27 a Katsina

-

Rundunar sojojin sama ta Najeriya (NAF), a karkashin rundunar FANSAN YANMA, ta samu babban nasara a jihar Katsina bayan kai farmaki na sama da ya hallaka wasu ‘yan bindiga a ƙaramar hukumar Faskari

 

Zagazola ya samu labarin cewa an gudanar da farmakin ne a safiyar 1 ga watan Fabrairu, inda aka kai hari kan sansanonin da ake zargin ‘yan bindiga suna taruwa a dajin Shawu–Mununu Ruwan Godiya a yankin faskari.

 

Majiyoyi sun ce farmakin ya biyo bayan dogon bincike na sama da ya tabbatar da kasancewar ‘yanbindiga masu makamai a yankin Bakori–Guga, waɗanda ake zargi da kai hare-hare kwanan nan.

 

An yi kira ga al’umma da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga hukumomi domin taimaka musu wajen gano motsin ‘yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular