HomeSashen Hausa'Yanta'adda Sun Kai Hari Ayarin 'Yan Ɗaurin Aure, Sun Sace Amarya a...

‘Yanta’adda Sun Kai Hari Ayarin ‘Yan Ɗaurin Aure, Sun Sace Amarya a Jihar Katsina

-

‘Yan ta’adda a jihar Katsina, sun kai hari inda suka kashe wasu mahalarta ɗaurin aure, tare da sace amarya da wasu mutane 17.

 

Nigerian Post ta bibiyi Rahotan Alfijir Radio da cewa, Harin ya faru ne a yankin Unguwar Nagunda da ke ƙaramar Hukumar Ƙanƙara, washegarin da gwamnatin jihar ta bayyana dalilan shirinta na sakin mutum 70 da ake zargi da laifukan ta’addanci a faɗin jihar.

 

Sai de, daga bisani mutum 8 daga cikin waɗanda aka sace sun samu kuɓuta, inda suka koma wurin iyalansu a ranar Litinin.

 

Kazalika ‘yan bindiga sun kashe wani mutum a ƙauyen Kafa da ke kan babbar hanyar Kankara zuwa Sheme da ke ƙaramar hukumar Ƙanƙara a jihar Katsina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Raɗɗa Khadimul Tauhid the First: 20 Years After, How the Governor Offers a Helping Hand to New Islamic Converts

Dikko Raɗɗa Khadimul Tauhid the First: 20 Years After, How the Governor Offers a Helping Hand to New Islamic Converts By Usman Salisu Gurbin Mikiya Since his...

Most Popular