HomeSashen HausaZa mu ƙarar da 'Yanbindiga a shekara ɗaya idan har Gwamnati za...

Za mu ƙarar da ‘Yanbindiga a shekara ɗaya idan har Gwamnati za ta goya mana baya– inji CJTF

-

Haɗakar Jami’an Tsaron Sa-kai na Ƙasa (CJTF) ta ci alwashin karar da ƴanbindiga da ke addabar wasu sassa na Arewacin Nijeriya a cikin shekara ɗaya take.

 

Farfesa Kailani Muhammad, Shugaban CJTF na Ƙasa ne ya baiyana hakan yayin da Charles Omini, Jakadan Musamman na Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam na Afrika ta Yamma ya mika masa takardar zama ɗan hadaddiyar kungiyar jami’an sa-kai ta Afirka ta Yamma (JTF) a Abuja a ranar Asabar.

 

A cewar Muhammad, da Gwamnatin Tarayya ta ba da ƙarfi tare da tallafa wa CJTF kayan aiki,’ da suka dace to za su murƙushe ’yan bindiga cikin shekara guda.

 

Ya yi kira ga gwamnati da ta ba Civilian JTF goyon bayan da ya dace domin su nuna abin da za su iya yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Gwamnatin Gombe Ta Bai Wa Iyalan ’Yanjarida 7 Da Suka Rasu Tallafin Miliyan 14

Gwamnatin Jihar Gombe ta raba naira miliyan 14 ga iyalan ’yan jarida bakwai da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya faru a...

‎Gidauniyar Dahiru Mangal, Ta Yiwa Mutane 18,000 Aikin Ido Kyauta A Katsina

‎Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta...

Most Popular