HomeSashen HausaTsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu...

Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu A Najeriya

-

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu daga Aminiya, an tabbatar da cewa, tsofaffin ma’aikatan (FRCN) Federal Radio Corporation of Nigeria (FRCN) sun ce sun shirya gudanar zanga-zanga tsirara a gobe Litinin 8 ga Disamba na shekarar 2025.

 

Shugaban ƙungiyar, Mista Mukaila Ogunbote, shi ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce za su shiga zanga-zangar ne domin maƙalewar wasu haƙƙoƙinsu da gwamnati ta gaza biya kamar yadda sakataren kuɗi na ƙungiyar tsofaffin ma’aikatan, Bola Popoola ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a Legas.

 

Sun jaddada cewa, lamarin ya kai su bango ne shiyasa suke ƙoƙarin gudanar da zanga-zangar ko Gwamnatin tarayya za ta waiwayo a garesu.

 

Wannan dai, ba shi ne karon farko da ‘yan ƙasa gamida masu aiki a ƙasar ke yawan yin barazana na yin zanga-zanga a Najeriya, wanda ko a makonnin da suka gaba ASSUU ta yi Barazanar tsunduma yajin aiki jim kadan bayan da suka gama jan kunne ga wata zanga-zangar lumana a yankunan ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular