HomeSashen HausaAn ƙaddamar da sabbin jami'ai da za su rinƙa ba 'Yansanda bayanai...

An ƙaddamar da sabbin jami’ai da za su rinƙa ba ‘Yansanda bayanai a Katsina

-

Babban uba ga PCRC Alhaji Sabo Musa, ya jagoranci ƙaddamar da sabbin jami’ai da za su rinƙa ba ‘Yandanda bayanai a ƙananan hukumomi 8, da suka haɗa da Dandume, ƙaramar hukumar Katsina, Dutsinma, da sauran su.

Majiyar ta samu cewa, an kaddamar da su ne domin bada bayanai a kowacce Unguwa a jihar, da kuma kashe duk wasu fitintinu a cikin unguwanni, idan abin kuma ya fi karfinsu su kai rahota ga manyan jami’an tsaro.

Lokacin da ake ƙaddamar da su, masu ruwa da tsaki na ɓangaren tsaro a jihar Katsina sun ziyarci taron, domin haɗa kai da duk wani sashe na jami’an tsaro a jihar.

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu, lokacin da ake ƙaddamar da shuwagabannin jami’an a jihar, Alhaji Sabo Musa, shi ne a ƙaddamar da su a ranar Lahadi da ta gaba a birnin Katsina.

An kuma ja kunnen su da su kasance ma su gaskiya da amana ba tare da sun ci amanar yankunan su ba ko kuma karya dokar da ta shafi ƙasa, an ce ma su, ya zama wajibi su bi doka da oda kar su kasance sun tauye haƙƙin wasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular