HomeSashen HausaNafi Son Cigaban Ƙasa A Kan Kowanne Muradi Na Kaina- Inji Sule...

Nafi Son Cigaban Ƙasa A Kan Kowanne Muradi Na Kaina- Inji Sule Lamido

-

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya bayyana cewa a shirye yake ya goyi bayan kowanne irin tsarin siyasa da zai kawo tsaro da zaman lafiya a Najeriya, musamman ma kafin zaɓen 2027. A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, 23 ga watan Yuli, 2025, Lamido ya nuna cewa babban burinsa shi ne haɗin kan ƙasa da kwanciyar hankali, ba wai cika muradinsa na siyasa kawai ba.

Ya ce, duk da cewa har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP, bai hana shi yin aiki tare da wasu ƙungiyoyi ko shugabannin siyasa da nufin taimaka wa ƙasar idan hakan zai amfani Najeriya baki ɗaya.
Lamido ya ƙaryata maganganun da aka yaɗawa na cewa yana shirin barin PDP musamman zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), inda ya tabbatar da cewa biyayyarsa ga PDP na nan.

Amma ya shaida cewa yana ganin akwai bukatar ‘yan siyasa su yi haɗin kai duk da bambancin jam’iyya domin magance matsaloli kamar rashin tsaro, yunwa, da rikice-rikicen cikin gida. Ya ce, “Ko da na zauna a PDP, ƙofa abuɗe take ga duk wata hanya da za ta tabbatar da tsaron Najeriya, zaman lafiyar tare da cigaba.”

Har ila yau, ya gargadi cewa kawai ƙirƙirar sabbin jihohi ko canza iyakoki wanda hakan ba zai warware matsalolin ƙasar nan na dindindin ba.

Dangane da ziyarar siyasa da aka yi kwanan nan, musamman haɗuwar Sanata Kwankwaso da Shugaba Tinubu, Lamido ya bayyana cewa kowanne ɗan siyasa na da ‘yancin yanke irin wannan shawarar kuma babu laifi a yin hakan.

Ya ƙara da cewa ‘yan siyasa yana da kyau su fifita amfanin ƙasa sama da rigingimu na jam’iyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular