HomeSashen HausaNafi Son Cigaban Ƙasa A Kan Kowanne Muradi Na Kaina- Inji Sule...

Nafi Son Cigaban Ƙasa A Kan Kowanne Muradi Na Kaina- Inji Sule Lamido

-

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya bayyana cewa a shirye yake ya goyi bayan kowanne irin tsarin siyasa da zai kawo tsaro da zaman lafiya a Najeriya, musamman ma kafin zaɓen 2027. A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, 23 ga watan Yuli, 2025, Lamido ya nuna cewa babban burinsa shi ne haɗin kan ƙasa da kwanciyar hankali, ba wai cika muradinsa na siyasa kawai ba.

Ya ce, duk da cewa har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP, bai hana shi yin aiki tare da wasu ƙungiyoyi ko shugabannin siyasa da nufin taimaka wa ƙasar idan hakan zai amfani Najeriya baki ɗaya.
Lamido ya ƙaryata maganganun da aka yaɗawa na cewa yana shirin barin PDP musamman zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), inda ya tabbatar da cewa biyayyarsa ga PDP na nan.

Amma ya shaida cewa yana ganin akwai bukatar ‘yan siyasa su yi haɗin kai duk da bambancin jam’iyya domin magance matsaloli kamar rashin tsaro, yunwa, da rikice-rikicen cikin gida. Ya ce, “Ko da na zauna a PDP, ƙofa abuɗe take ga duk wata hanya da za ta tabbatar da tsaron Najeriya, zaman lafiyar tare da cigaba.”

Har ila yau, ya gargadi cewa kawai ƙirƙirar sabbin jihohi ko canza iyakoki wanda hakan ba zai warware matsalolin ƙasar nan na dindindin ba.

Dangane da ziyarar siyasa da aka yi kwanan nan, musamman haɗuwar Sanata Kwankwaso da Shugaba Tinubu, Lamido ya bayyana cewa kowanne ɗan siyasa na da ‘yancin yanke irin wannan shawarar kuma babu laifi a yin hakan.

Ya ƙara da cewa ‘yan siyasa yana da kyau su fifita amfanin ƙasa sama da rigingimu na jam’iyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Nijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso,...

Duniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa a Najeriya, Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taɓa bari Najeriya ta ruguje a hannunta ba, komai rintsi.   Kamar yadda...

Most Popular