HomeSashen HausaFulani Na Ƙoƙarin Ƙwace Garuruwa Da Kuma Gonaki A Yankin Dukku Da...

Fulani Na Ƙoƙarin Ƙwace Garuruwa Da Kuma Gonaki A Yankin Dukku Da Darazo A Jihar Gombe

-

Rahotannin sun bayyana cewa, wasu Fulani suna ƙoƙarin ƙwace wasu garuruwa da ke tsakanin kan iyakar ƙananan hukumomin Dukku (Jihar Gombe) da Darazo (Jihar Bauchi).

Shaidun gani da ido da suka fito daga yankin, su ne suka tabbatar da faruwar lamarin, inda suka ce, fulanin sun tarwatsa al’ummar garin Yau Tare, inda suka ka umarce su da su gaggauta barin garin.

Kamar yadda Nigerian Post ta bibiyi rahoton, dalilin hakan ne ya sa ma zauna garin suka fara ƙaura nan take, bayan sun kashe wani a yayin da suka kai hari garin.

Haka zalika, sun shiga wasu garuruwa kamar Jamari, Dukkuyel a ranakun Kasuwa, inda suka dinga dukkan mutane babu wani dalili.

Tuni dai aka tabbatar da faruwar lamarin, inda aka kara jaddada cewa, Fulanin na yawo tsakanin Yau Tare, Hashidu, Malala, Jamari Dukkuyel da wasu garuruwa, wanda hakan ya jefa al’umma cikin tashin hankali da gudun hijira.

Haka zalika, sun bayyana aniyarsu ta amfani da gonakin al’ummar yankin, lamarin da ya ƙara tayar da hankalin manoma da iyalai.

Rahotanni kuma na cewa, ana zargin Fulanin da gayyato abokan su daga wasu sassa daban-daban na ƙasar nan domin ƙara ƙarfi, yanzu haka sun sauka cikin dajin Darazo.

Saboda haka ake kira ga gwamnatocin jihohin Gombe da Bauchi da su gaggauta ɗaukar mataki na musamman, domin kare rayuka, gonaki da dukiyoyin jama’a a wannan yanki kafin lamura su rikide zuwa rikicin da zai fi ƙarfin Gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Gwamnan Katsina Ya Zama Abin Koyi Ga Sauran Jihohin Najeriya— Inji Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya zama abin koyi idan akai duba da...

Budurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren Dole

Wata matashiya ta kashe kanta a karamar hukumar Gubio ta jihar Borno, bayan mahaifinta ya tilasta mata aure da ɗaya daga cikin abokansa.   Shafin jaridar Zagazola...

Most Popular