HomeSashen HausaTinubu Ya Yafewa Maryam Sanda Bayan An Yanke Ma Ta Hukunci Kisa...

Tinubu Ya Yafewa Maryam Sanda Bayan An Yanke Ma Ta Hukunci Kisa A 2020

-

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa — matar da aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2020 bayan samunta da laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello.

Maryam Sanda, mai shekaru 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas tana tsare a gidan gyaran hali na Suleja kafin wannan afuwa daga shugaban ƙasa.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan shawarar kwamitin shugaban ƙasa kan yafewa fursunoni da masu laifi bayan nazarin takardun shari’arsu da yanayin da suke ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Gwamnan Katsina Ya Zama Abin Koyi Ga Sauran Jihohin Najeriya— Inji Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya zama abin koyi idan akai duba da...

Budurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren Dole

Wata matashiya ta kashe kanta a karamar hukumar Gubio ta jihar Borno, bayan mahaifinta ya tilasta mata aure da ɗaya daga cikin abokansa.   Shafin jaridar Zagazola...

Most Popular