HomeSashen Hausa‎Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Yanke Jiki Ya Fadi Ana Tsaka Da Aikin...

‎Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Yanke Jiki Ya Fadi Ana Tsaka Da Aikin Ofis

-

Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, ya yanke jiki ya fadi yayin da yake tsaka da gudanar da ayyukansa a ofis ɗinsa da ke Gidan Gwamnati, Yenagoa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

‎Shaidu daga fadar gwamnati sun ce lamarin ya faru ne ba wani manuniyar cewa yana da wata rashin lafiya, lamarin da ya jefa ma’aikatan ofishin cikin tashin hankali.

‎Rahotanni sun tabbatar da cewa an gaggauta kai Mataimakin Gwamnan zuwa Babban Asibitin Tarayya da ke Yenagoa (Federal Medical Centre) domin kula da lafiyarsa.

‎Duk da cewa hukumomin jihar ba su fitar da cikakken bayanin halin da yake ciki ba tukuna, majiyoyi sun ce likitoci suna ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da ya farfaɗo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Dangote Ya Buƙaci a Binciki Shugaban NMDPRA Kan Zargin Ɓarnatar Da Kuɗaɗe ‎

Hamshakin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aliko Dangote, ya yi kira da a gudanar da bincike kan Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur na Ƙasa (NMDPRA),...

An Ƙone Wata Matar Aure Da Ɗanta A Kano 

Mazauna unguwar Sheka Sabuwar Gandu da ke cikin birnin Kano, sun shiga firgici a ranar Lahadi bayan kisan wata mata mai juna biyu da ɗanta...

Most Popular