HomeLabarai‎Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Yanke Jiki Ya Fadi Ana Tsaka Da Aikin...

‎Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Yanke Jiki Ya Fadi Ana Tsaka Da Aikin Ofis

-

Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, ya yanke jiki ya fadi yayin da yake tsaka da gudanar da ayyukansa a ofis ɗinsa da ke Gidan Gwamnati, Yenagoa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

‎Shaidu daga fadar gwamnati sun ce lamarin ya faru ne ba wani manuniyar cewa yana da wata rashin lafiya, lamarin da ya jefa ma’aikatan ofishin cikin tashin hankali.

‎Rahotanni sun tabbatar da cewa an gaggauta kai Mataimakin Gwamnan zuwa Babban Asibitin Tarayya da ke Yenagoa (Federal Medical Centre) domin kula da lafiyarsa.

‎Duk da cewa hukumomin jihar ba su fitar da cikakken bayanin halin da yake ciki ba tukuna, majiyoyi sun ce likitoci suna ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da ya farfaɗo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Atletico Knock Out Barcelona to Secure First Semifinal Spot in Eight Years

Atlético Madrid reached the semifinals for the first time since 2017 after knocking out FC Barcelona. Barcelona started the match strongly, with Lamine Yamal and Ferran...

FG Denies ADC Use of Eagle Square for Abuja Convention

The African Democratic Congress (ADC) has said it was denied access to both Eagle Square and the Moshood Abiola National Stadium for its planned national...

Most Popular