HomeSashen HausaSabon Rikici Ya Kunno Kai a Katsina United Saboda Rashin Biyan Albashin...

Sabon Rikici Ya Kunno Kai a Katsina United Saboda Rashin Biyan Albashin Watanni Biyar

-

Rikicin da ke damun Katsina United ya kara kamari jiya da yamma, bayan da ‘yan wasan kulob ɗin suka gudanar da zanga-zangar neman a biya su albashin watanni biyar da suka dade suna bi.

 

Majiyarmu ta jaridar the Nation ra ruwaito cewa Lamarin ya faru ne jim kadan kafin fafatawa mako na 16 a Gasar NPFL da Bendel Insurance, wadda suka sha kashi 1–0 daga baya.

 

Rikicin ya faru ne a sansanin su na Ilorin, inda ‘yan wasan da suka gaji da jinkiri suka hana motar su ta tashi zuwa filin wasa na George Innih, Ilorin — wurin da zasu buga wasan.

Yan’wasa da suka gudanar da zanga-zangar sun nace cewa ba za su fito wasa ba sai an warware batun bashin albashin da suke bin kulob ɗin, wanda wasu daga cikinsu ke cewa tun farkon kakar bana ake binsu.

 

Wannan takaddama ta tilasta wa jami’an kulob ɗin shirin gaggawa, inda a ƙarshe suka samo wata mota daban domin kai ‘yan wasan da ake da su zuwa filin wasa.

Bendel Insurance ta yi amfani da wannan rudani, inda a minti na 72 Elmer Arunta ya zura kwallo cikin natsuwa, wanda ya tabbatar musu da nasarar farko a waje a wannan kakar tare da ficewa daga yankin waɗanda ke fuskantar faduwa rukuni.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da...

Most Popular