HomeSashen HausaZanga-zangar Adawa Da Juyin Mulki Ta Ɓarke A Guinea-Bissau

Zanga-zangar Adawa Da Juyin Mulki Ta Ɓarke A Guinea-Bissau

-

Daruruwan ‘yan Guinea-Bissau sun yi tattaki a cikin birnin Bissau, babban birnin ƙasar, domin yin zanga-zanga kan juyin mulkin soja da aka yi a watan da ya gabata tare da neman a saki shugabannin ‘yan adawa.

 

Masu zanga-zangar sun yi arangama da jami’an tsaro a ranar Juma’a yayin da suke kiran a saki Domingos Pereira, shugaban Jam’iyyar African Party for the Independence of Guinea and Cape Verde (PAIGC), wanda rahotanni suka ce an tsare shi ne a lokacin juyin mulkin.

 

Jami’an soji sun sanar da juyin mulki a ƙasar da ke Yammacin Afirka mai amfani da harshen Fotigal, kwanaki kaɗan bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, kuma ‘yan sa’o’i kaɗan kafin a ayyana sakamakon zaɓen.

 

Shugaba Umaro Embaló da babban abokin hamayyarsa, Fernando Dias da Costa, duk sun ayyana kansu a matsayin waɗanda suka yi nasara tun kafin hukumar zaɓe ta sanar da sakamakon.

 

Daga bisani, ‘yan juyin mulkin sun naɗa Manjo Janar Horta Inta-a a matsayin shugaban riƙo.

 

Bayan juyin mulkin, Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta dakatar da Guinea-Bissau daga ƙungiyar har sai an dawo da tsarin mulki a ƙasar.

 

Ƙungiyar ta bayyana wannan mataki ne a cikin wata sanarwa bayan kiran wani taron gaggawa na shugabannin ƙasashe da gwamnatoci ta kafar intanet kan halin da ake ciki.

 

Ana sa ran shugabannin yankin za su gana a ranar Lahadi domin tattauna rikicin da kuma ɗaukar matakan takunkumi masu yuwuwa kan ƙasar ta Yammacin Afirka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Governor Dikko Radda Inaugurates Katsina State Council of Emir’s

Katsina State Governor has inaugurated the State Council of Emirs with the Emir of Katsina Alhaji Abdulmumini Kabir as the Chairman while his Daura counterpart...

SUBEB Chairman Reiterates Need for Compliance with Minimum Standards for School Infrastructure in Katsina

Executive Chairman Katsina State Universal Board has restated necessity of complying Minimum Standard for Schools' Infrastructure in the state.   Dr. Kabir Magaji Gafiya stated this during...

Most Popular