HomeSashen HausaAmurka Da Najeriya Na Dab da Cimma Yarjejeniyar Tsarin Tsaro Don Yakar...

Amurka Da Najeriya Na Dab da Cimma Yarjejeniyar Tsarin Tsaro Don Yakar Boko Haram da ISIS

-

Danmajalisar wakilan Amurka, Riley Moore, ya ce Amurka da Najeriya na dab da cimma matsaya kan wani tsarin tsaro na dabaru da nufin yaƙar Boko Haram da ISIS a Najeriya.

 

Moore, wanda ya kai ziyara Najeriya tare da wasu ’yan majalisar Amurka, ya bayyana cewa sun yi tattaunawa masu kyau da gwamnatin Najeriya kan batutuwan tsaro.

 

Ya ce ziyarar ta ba shi damar ganawa da wasu daga cikin waɗanda ta’addanci ya shafa, inda ya ce abin da ya gani ya girgiza zuciya.

 

Dan majalisar ya kuma ce zai miƙa rahoto ga Shugaban Amurka, Donald Trump, domin bayyana hanyoyin da za a bi wajen haɗa kai da gwamnatin Najeriya don kawo ƙarshen kashe-kashen da ake dangantawa da ta’addanci.

 

A yayin ziyarar, tawagar ta gana da Mai Ba da Shawara kan Tsaron Kasa, Nuhu Ribadu, a Abuja, tare da ziyartar wasu al’ummomi a arewacin Najeriya.

 

Moore na daga cikin ’yan siyasar Amurka da ke ikirarin ana tsananta wa Kiristoci a Najeriya, kuma a ranar 7 ga Nuwamba ya gabatar da kuduri a majalisar wakilan Amurka kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da...

Most Popular