HomeSashen HausaBan Da Alƙalai A Jerin Waɗanda Za a Cire Wa 'Yansandan Da...

Ban Da Alƙalai A Jerin Waɗanda Za a Cire Wa ‘Yansandan Da Ke Ba Su Kariya a Najeriya– Inji Alkalin Alkalai

-

Babbar Mai Shari’a ta Nijeriya, Justice Kudirat Kekere-Ekun, ta bayyana cewa umarnin Shugaban kasa na janye jami’an ‘yan sanda da ke aiki a matsayin masu gadin Manyan Mutane (VIPs) na daga cikin matakan da gwamnati ke dauka domin dakile karuwar matsalar rashin tsaro a kasar.

Ta bayyana hakan ne a matsayin wani bangare na kokarin mayar da karfin ‘yan sanda inda ya fi dacewa, musamman wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin Nijeriya.

Sai dai mai taimaka wa Babbar Mai Shari’a ta Nijeriya kan harkokin yada labarai, Tobi Soniyi, ya bayyana cewa wannan umarni ba ya shafar alkalai, inda ya jaddada cewa tsaron masu shari’a bai shiga cikin wannan mataki ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Dangote Ya Buƙaci a Binciki Shugaban NMDPRA Kan Zargin Ɓarnatar Da Kuɗaɗe ‎

Hamshakin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aliko Dangote, ya yi kira da a gudanar da bincike kan Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur na Ƙasa (NMDPRA),...

An Ƙone Wata Matar Aure Da Ɗanta A Kano 

Mazauna unguwar Sheka Sabuwar Gandu da ke cikin birnin Kano, sun shiga firgici a ranar Lahadi bayan kisan wata mata mai juna biyu da ɗanta...

Most Popular