HomeSashen Hausa‎Dangote Ya Buƙaci a Binciki Shugaban NMDPRA Kan Zargin Ɓarnatar Da Kuɗaɗe...

‎Dangote Ya Buƙaci a Binciki Shugaban NMDPRA Kan Zargin Ɓarnatar Da Kuɗaɗe ‎

-

Hamshakin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aliko Dangote, ya yi kira da a gudanar da bincike kan Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur na Ƙasa (NMDPRA), Farouk Ahmed, bisa zargin ɓarnatar da dukiyar jama’a da kuma cutar da tattalin arzikin ƙasa.

‎Dangote ya bayyana cewa ko shi da irin arzikin da Allah ya hore masa, ba zai iya biyan kuɗin karatun sakandaren ’ya’yansa da ya haura Naira biliyan bakwai ba. Ya ce irin wannan adadi na kuɗi ya wuce tunanin biyan kuɗin makaranta a matakin sakandare.

‎Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, ya yi wannan furuci ne cikin wani bidiyo da ya raba wa manema labarai, wanda ya yaɗu a shafukan sada zumunta a ƙarshen makon da ya gabata.

‎A cewarsa, “Shugaban Hukumar Man Fetur ta NMDPRA, Farouk Ahmed, na biyan kuɗin makarantar sakandaren ’ya’yansa har dala miliyan biyar a Switzerland.”

‎Wannan furuci ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a, inda da dama ke kira ga hukumomi da su yi cikakken bincike domin tabbatar da gaskiyar zarge-zargen da kuma kare muradun tattalin arzikin ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kwamishinan ’Yansanda Ya Karɓi Baƙuncin Sabon Kwamandan Rundunar Sojin Saman Najeriya Da Aka Turo Katsina

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Katsina, CP Bello Shehu, MNIM, ya karɓi bakuncin sabon Kwamandan da aka turo na Rundunar Sojin Sama ta Najeriya, 213...

Tsohon gwamnan Sokoto Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya koma jam’iyar APC

Bafarawa da magoya bayansa sun bayyana komawa jam'iyar APC a babban xakin taro na gidansa dake jihar Sakkwato a ranar Laraba.   Tsohon Gwamnan ya ce magoya...

Most Popular