HomeLabarai‎Dangote Ya Buƙaci a Binciki Shugaban NMDPRA Kan Zargin Ɓarnatar Da Kuɗaɗe...

‎Dangote Ya Buƙaci a Binciki Shugaban NMDPRA Kan Zargin Ɓarnatar Da Kuɗaɗe ‎

-

Hamshakin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aliko Dangote, ya yi kira da a gudanar da bincike kan Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur na Ƙasa (NMDPRA), Farouk Ahmed, bisa zargin ɓarnatar da dukiyar jama’a da kuma cutar da tattalin arzikin ƙasa.

‎Dangote ya bayyana cewa ko shi da irin arzikin da Allah ya hore masa, ba zai iya biyan kuɗin karatun sakandaren ’ya’yansa da ya haura Naira biliyan bakwai ba. Ya ce irin wannan adadi na kuɗi ya wuce tunanin biyan kuɗin makaranta a matakin sakandare.

‎Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, ya yi wannan furuci ne cikin wani bidiyo da ya raba wa manema labarai, wanda ya yaɗu a shafukan sada zumunta a ƙarshen makon da ya gabata.

‎A cewarsa, “Shugaban Hukumar Man Fetur ta NMDPRA, Farouk Ahmed, na biyan kuɗin makarantar sakandaren ’ya’yansa har dala miliyan biyar a Switzerland.”

‎Wannan furuci ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a, inda da dama ke kira ga hukumomi da su yi cikakken bincike domin tabbatar da gaskiyar zarge-zargen da kuma kare muradun tattalin arzikin ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Brazil Doesn’t Necessarily Have to Win the World Cup –Vinícius

Renowned Brazilian footballer Vinícius Júnior stated that his country does not necessarily have to be among the teams that win the 2026 FIFA World Cup. He...

OMOS Continues to Fly Nigeria’s Flag High in WWE

Renowned wrestling star Omos continues to represent Nigeria on the global stage of WWE, where he stands among the tallest athletes in the world. Omos has...

Most Popular