HomeSashen Hausa'Yan'ta'adda Za Su Ɗandana Kuɗar Su Kan Harin Bom a masallacin Jihar...

‘Yan’ta’adda Za Su Ɗandana Kuɗar Su Kan Harin Bom a masallacin Jihar Borno– Inji Shettima

-

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya yi Allah-wadai da harin bam da ya afku a wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, Jihar Borno, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da jikkata wasu da dama.

 

Shettima ya bayyana cewa waɗanda suka aikata harin ba za su tsira ba, inda ya tabbatar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ƙara tsaurara matakan tsaro a jihar bayan faruwar lamarin.

 

A wata sanarwa da ya fitar, Mataimakin Shugaban kasar ya ce gwamnatin tarayya na tura ƙarin jami’an tsaro na musamman domin bin sawu da kama masu hannu a harin, yana mai cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙuri na kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron ƙasa ba.

 

Ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Borno da iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken goyon baya domin murkushe ta’addanci, musamman a yankin Arewa maso gabas.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Abinda Ya Faru Da Ni Ya Zame Min Alkhairi– Malam Bala Dorayi

Malam Bala Dorayi, wanda aka fi sani da Sarkin Yakin Karyar Ƙasar Hausa, ya bayyana cewa abin da ya faru da shi a baya kaddara...

‎Kim Jong Un Ya Zaɓi Ƴarsa Mai Shekara 13 a Matsayin Wadda Za Ta Gaje Shi ‎

Rahotanni daga National Intelligence Service (NIS) sun bayyana cewa shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un, ya zaɓi ƴarsa mai shekara 13, Kim Ju Ae,...

Most Popular