HomeSashen Hausa'Yan'ta'adda Za Su Ɗandana Kuɗar Su Kan Harin Bom a masallacin Jihar...

‘Yan’ta’adda Za Su Ɗandana Kuɗar Su Kan Harin Bom a masallacin Jihar Borno– Inji Shettima

-

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya yi Allah-wadai da harin bam da ya afku a wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, Jihar Borno, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da jikkata wasu da dama.

 

Shettima ya bayyana cewa waɗanda suka aikata harin ba za su tsira ba, inda ya tabbatar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ƙara tsaurara matakan tsaro a jihar bayan faruwar lamarin.

 

A wata sanarwa da ya fitar, Mataimakin Shugaban kasar ya ce gwamnatin tarayya na tura ƙarin jami’an tsaro na musamman domin bin sawu da kama masu hannu a harin, yana mai cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙuri na kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron ƙasa ba.

 

Ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Borno da iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken goyon baya domin murkushe ta’addanci, musamman a yankin Arewa maso gabas.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎DA DUMI-DUMI: Rikici Ya Ɓarke A Sabuwar Unguwa Katsina, Mutum 1 Ya Rasu, Matasa Sun Cinna Wuta a Ofisoshin Tsaro

‎A daren jiya zuwa safiyar yau, an samu tashin hankali a Sabuwar Unguwar Kofar Kaura, lamarin da ya janyo hankalin al’umma tare da haifar da...

‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam’iyyar NNPP

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya amince da bai wa ’ya’yan ’yan Majalisar Jiha biyu da suka rasu, damar tsayawa takara, domin neman...

Most Popular