HomeSashen Hausa'Yan'ta'adda Za Su Ɗandana Kuɗar Su Kan Harin Bom a masallacin Jihar...

‘Yan’ta’adda Za Su Ɗandana Kuɗar Su Kan Harin Bom a masallacin Jihar Borno– Inji Shettima

-

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya yi Allah-wadai da harin bam da ya afku a wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, Jihar Borno, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da jikkata wasu da dama.

 

Shettima ya bayyana cewa waɗanda suka aikata harin ba za su tsira ba, inda ya tabbatar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ƙara tsaurara matakan tsaro a jihar bayan faruwar lamarin.

 

A wata sanarwa da ya fitar, Mataimakin Shugaban kasar ya ce gwamnatin tarayya na tura ƙarin jami’an tsaro na musamman domin bin sawu da kama masu hannu a harin, yana mai cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙuri na kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron ƙasa ba.

 

Ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Borno da iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken goyon baya domin murkushe ta’addanci, musamman a yankin Arewa maso gabas.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular