HomeSashen HausaNajeriya Ta Tabbatar Da Harin Amurka Kan ‘Yan Ta’adda a Sokoto

Najeriya Ta Tabbatar Da Harin Amurka Kan ‘Yan Ta’adda a Sokoto

-

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da cewa Najeriya na ci gaba da haɗin gwiwar tsaro cikin tsari da ƙasashen duniya, ciki har da Amurka, domin fuskantar barazanar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi ta hanyar amfani da tashin hankali.

 

Ma’aikatar harkokin waje ta bayyana hakan a ranar Alhamis, bayan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sanar da cewa sojojin Amurka sun kai hare-haren sama kan wuraren ‘yan ta’adda a Najeriya.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa, ya fitar, gwamnatin ta tabbatar da cewa harin ya haifar da “kai munanan hare-haren sama na musamman kan wuraren ‘yan ta’adda a Arewa maso yammacin Najeriya.”

 

Ma’aikatar ta ce wannan haɗin gwiwa da Amurka da sauran abokan hulɗa na bin ka’idojin hulɗar ƙasa da ƙasa da yarjejeniyoyin bangarori biyu, kuma ya haɗa da musayar bayanan sirri, daidaiton dabarun tsaro, da sauran tallafi da suka dace da dokokin ƙasa da ƙasa tare da mutunta ikon mulkin Najeriya.

 

Ebienfa ya jaddada cewa dukkan matakan yaki da ta’addanci na Najeriya suna karkata ne wajen kare rayukan fararen hula, kiyaye haɗin kan ƙasa, da kuma mutunta haƙƙi da mutuncin dukkan ‘yan ƙasa ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎DA DUMI-DUMI: Rikici Ya Ɓarke A Sabuwar Unguwa Katsina, Mutum 1 Ya Rasu, Matasa Sun Cinna Wuta a Ofisoshin Tsaro

‎A daren jiya zuwa safiyar yau, an samu tashin hankali a Sabuwar Unguwar Kofar Kaura, lamarin da ya janyo hankalin al’umma tare da haifar da...

‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam’iyyar NNPP

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya amince da bai wa ’ya’yan ’yan Majalisar Jiha biyu da suka rasu, damar tsayawa takara, domin neman...

Most Popular