HomeSashen HausaJirgin Ƙasan Kaduna–Abuja Ya Samu Tangardar Na‘ura a Rijana

Jirgin Ƙasan Kaduna–Abuja Ya Samu Tangardar Na‘ura a Rijana

-

Fasinjoji da dama sun shafe sa’o’i suna jiran gyara bayan jirgin kasa na Kaduna zuwa Abuja da ya samu matsala a kusa da kauyen Rijana a ranar Litinin.

 

Rahotanni daga Daily Trust sun ce jirgin ya tashi daga Kaduna da misalin karfe 2:30 na rana, amma ya lalace a hanya, lamarin da ya jinkirta tafiyar da aka saba kammalawa cikin kusan sa’o’i biyu da rabi.

 

Majiyoyi sun ce matsalar ta tilasta wa jirgin tsayawa na dogon lokaci yayin da aka yi kokarin gyara shi kafin a ci gaba da tafiya.

 

Manajan tashar jirgin kasa ta Abuja na Hukumar NRC, Mista Modibbo, ya tabbatar da faruwar lamarin a sakon WhatsApp da ya aike ranar Litinin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Matashiya ‘Yar Shekara 18 Daga Katsina, Ta Haddace Al-qur’ani Maigirma ‎

Wata matashiya mai suna Amina Usman, ƴar shekara 18 daga Jihar Katsina, ta samu nasarar Saukar Alƙur'ani Mai Girma a shekarar da ta gabata. ‎ A jiya,...

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

Most Popular