Fasinjoji da dama sun shafe sa’o’i suna jiran gyara bayan jirgin kasa na Kaduna zuwa Abuja da ya samu matsala a kusa da kauyen Rijana a ranar Litinin.
Rahotanni daga Daily Trust sun ce jirgin ya tashi daga Kaduna da misalin karfe 2:30 na rana, amma ya lalace a hanya, lamarin da ya jinkirta tafiyar da aka saba kammalawa cikin kusan sa’o’i biyu da rabi.
Majiyoyi sun ce matsalar ta tilasta wa jirgin tsayawa na dogon lokaci yayin da aka yi kokarin gyara shi kafin a ci gaba da tafiya.
Manajan tashar jirgin kasa ta Abuja na Hukumar NRC, Mista Modibbo, ya tabbatar da faruwar lamarin a sakon WhatsApp da ya aike ranar Litinin.
