HomeSashen HausaKotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Belin Abubakar Malami Ranar 7 Ga...

Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Belin Abubakar Malami Ranar 7 Ga Janairu

-

Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta ɗage sauraron shari’ar tsohon Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, zuwa ranar 7 ga Janairu, domin yanke hukunci kan bukatar belin da ya gabatar.

 

Abubakar Malami na fuskantar tuhume-tuhume na safarar kuɗi da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar a kansa. A halin yanzu, ana tsare da shi a gidan gyaran hali na Kuje tare da ɗansa, Abdulaziz Malami, da ɗaya daga cikin matansa, Bashir Asabe, waɗanda suma ake tuhuma a gaban kotun.

 

EFCC ta gurfanar da su ne bisa tuhume-tuhume guda 16, tana zarginsu da safarar kuɗaɗe da yawansu ya kai Naira biliyan 8.7.

 

Lokacin da aka karanto musu tuhume-tuhumen a ranar 29 ga Disambar 2025, dukkan waɗanda ake tuhumar sun musanta zargin da ake yi musu.

 

Kotun ta ce za ta bayyana matsayinta kan bukatar belin a ranar da aka sanya, yayin da ake ci gaba da tsare su har zuwa lokacin yanke hukuncin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Za Ta Karɓi Baƙuncin Mauludin Ƙasa na Inyass karo na Uku a Janairu 2026

An bukaci Gidan Rediyon Jihar Katsina da ya bayar da cikakken hadin kai da goyon baya wajen watsa dukkan ayyukan Mauludin Ƙasa na Inyass na...

‎Jirgin Marar Matuƙi Ya Faɗo a Dajin Kontagora, Jihar Neja

Wani jirgin marar matuƙi (drone) ya faɗo a wani daji da ke kusa da garin Kontagora, a Jihar Neja, da yammacin yau Juma'a, kamar yadda...

Most Popular