HomeSashen HausaKotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Belin Abubakar Malami Ranar 7 Ga...

Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Belin Abubakar Malami Ranar 7 Ga Janairu

-

Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta ɗage sauraron shari’ar tsohon Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, zuwa ranar 7 ga Janairu, domin yanke hukunci kan bukatar belin da ya gabatar.

 

Abubakar Malami na fuskantar tuhume-tuhume na safarar kuɗi da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar a kansa. A halin yanzu, ana tsare da shi a gidan gyaran hali na Kuje tare da ɗansa, Abdulaziz Malami, da ɗaya daga cikin matansa, Bashir Asabe, waɗanda suma ake tuhuma a gaban kotun.

 

EFCC ta gurfanar da su ne bisa tuhume-tuhume guda 16, tana zarginsu da safarar kuɗaɗe da yawansu ya kai Naira biliyan 8.7.

 

Lokacin da aka karanto musu tuhume-tuhumen a ranar 29 ga Disambar 2025, dukkan waɗanda ake tuhumar sun musanta zargin da ake yi musu.

 

Kotun ta ce za ta bayyana matsayinta kan bukatar belin a ranar da aka sanya, yayin da ake ci gaba da tsare su har zuwa lokacin yanke hukuncin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Raɗɗa Khadimul Tauhid the First: 20 Years After, How the Governor Offers a Helping Hand to New Islamic Converts

Dikko Raɗɗa Khadimul Tauhid the First: 20 Years After, How the Governor Offers a Helping Hand to New Islamic Converts By Usman Salisu Gurbin Mikiya Since his...

Most Popular