HomeSashen HausaKotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Belin Abubakar Malami Ranar 7 Ga...

Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Belin Abubakar Malami Ranar 7 Ga Janairu

-

Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta ɗage sauraron shari’ar tsohon Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, zuwa ranar 7 ga Janairu, domin yanke hukunci kan bukatar belin da ya gabatar.

 

Abubakar Malami na fuskantar tuhume-tuhume na safarar kuɗi da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar a kansa. A halin yanzu, ana tsare da shi a gidan gyaran hali na Kuje tare da ɗansa, Abdulaziz Malami, da ɗaya daga cikin matansa, Bashir Asabe, waɗanda suma ake tuhuma a gaban kotun.

 

EFCC ta gurfanar da su ne bisa tuhume-tuhume guda 16, tana zarginsu da safarar kuɗaɗe da yawansu ya kai Naira biliyan 8.7.

 

Lokacin da aka karanto musu tuhume-tuhumen a ranar 29 ga Disambar 2025, dukkan waɗanda ake tuhumar sun musanta zargin da ake yi musu.

 

Kotun ta ce za ta bayyana matsayinta kan bukatar belin a ranar da aka sanya, yayin da ake ci gaba da tsare su har zuwa lokacin yanke hukuncin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular