HomeSashen HausaGwamnatin Jihar Katsina Ta Horas Da Malamai 250 Da Faransifal 50, Don...

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Horas Da Malamai 250 Da Faransifal 50, Don Inganta Ilmin Jihar

-

Ma’aikatar Ilimi a Matakin Farko da na Sakandire a jihar Katsina, haɗin gwiwa da Majalisar Turai (British Council), ta ƙaddamar da wani muhimmin shirin horaswa ga Malamai da shugabannin makarantun Sakandire a jihar.

Taron gudana ranar Talata, 23 ga watan Satumba 2025, a babban ɗakin taro na KCK da ke cikin birnin Katsina.

Nigerian Post ta bibiyi cewa, Kwamishiniyar ilimi a Matakin Farko da na sakandare ta jihar Katsina, Hajiya Zainab Musa Musawa, ita ce ta jagoranci taron horas wa ga malaman na jihar Katsina.

Da take jawabi a wajen taron, Hajiya Zainab Musa Musawa ta jaddada cewa, gwamnatin jihar na ɗaukar ilimi a matsayin ginshiƙi na cigaban al’umma, kuma wannan shiri zai taimaka wajen inganta ayyukan Malamai da ɗalibai a jihar.

Kwamishinar ta ce shirin ya tanadi horaswa ga Malamai 250 da kuma shugabannin makarantun sakandiri 50, ƙarƙashin Shirin Ƙarfafa Harshen Turanci na Malamai wato Strengthening Teachers English Proficiency (STEP) da na koyar da shugabanci wato Instructional Leadership Programmes.

A cewar Kwamishiniyar, manufofin yin wannan taron horaswar shi ne domin inganta ƙwarewar malamai a ɓangaren harshen turanci, da tsara dabarun koyarwa ga shugabannin makarantu.

Ta yi ƙarin haske da cewa, da yawan malaman da aka horas za su Ƙarfafa harshen Turanci a Aji da kuma gabatar da dabarun Koyarwa.

Inda ta ƙara jaddada cewa, wannan horaswa na ɗaya daga cikin manyan matakan da gwamnatin jihar Katsina ke ɗauka domin tabbatar da ingantaccen ilimi a faɗin jihar.

Taron ya samu halartar jami’an Gwamnati, wakilai daga Majalisar Turai (British Council), shugabannin makarantu, da Malamai daga sassa daban-daban na jihar Katsina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular