HomeSashen HausaSojoji Sun Ceto Mutune 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A...

Sojoji Sun Ceto Mutune 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Tsanyawa, Jihar Kano

-

Sojojin Operation MESA da suka haɗa da jami’an Birgediya ta 3 ta rundunar sojin Najeriya, sojojin saman Najeriya da kuma ’yansanda sun ceto mutune bakwai da aka yi garkuwa da su yayin wani samame da suka kai da daddare a karamar hukumar Tsanyawa ta jihar Kano.

 

Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaron sun samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 11 na dare a ranar 29 ga Nuwamba 2025 kan harin ’yan bindiga a kauyen Yankamaye Cikin Gari. Sojojin da suka garzaya cikin gaggawa sun shiga musayar wuta da ’yan bindigar, waɗanda kafin isowarsu suka riga suka kashe wata mata ’yar kimanin shekara 60.

 

Bayan yin hargitsi da ’yan bindigar, sojojin sun bi sawun su zuwa hanyar Rimaye, inda suka ci gaba da musayar wuta kuma suka ƙwato waɗanda aka yi garkuwa da su. Sai dai mutane huɗu daga cikin waɗanda aka sace har yanzu ba a gan su ba.

 

Rahotoanni sun bayyana cewa ’yanbindigar sun tsere zuwa karamar hukumar Kankia ta jihar Katsina, kuma ana ci gaba da kokarin gano inda suke.

 

Kwamandan Birgediya ta 3 ya yabawa sojojin bisa jarumta da gaggawar da suka nuna, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci.

 

Sanarwar ta fito ne daga Babatunde Zubairu, Kyaftin kuma Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na rundunar soji, Birgediya ta 3.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sojojin Najeriya sun ceto ƴan mata 12 da aka sace a Askira/Uba da ke Jihar Borno

Rundunar Sojojin Najeriya ta ceto wasu ƴan mata 12 da ƴan Boko Haram/ISWAP suka sace a yankin Mussa da ke ƙaramar hukumar Askira/Uba, a jihar...

’Yan bindiga Sun Kashe Wata Mata Tare Da Sace Mutane 3 A Kano

Wasu ’yanbindiga dauke da makamai sun kai hari a kauyen Yankamaye da ke cikin Karamar Hukumar Tsanyawa a Jihar Kano, inda suka kashe wata mata...

Most Popular