HomeSashen HausaDuniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim...

Duniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim Shettima

-

Mataimakin Shugaban Ƙasa a Najeriya, Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taɓa bari Najeriya ta ruguje a hannunta ba, komai rintsi.

 

Kamar yadda Nigerian Post ta samu daga Aminiya, Shettima ya faɗi haka ne yayin da yake jawabi a wajen yaye ɗaliban Cibiyar Nazarin Manufofi da Muhimman Buƙatu ta Ƙasa (NIPSS) da ke Kuru a Jihar Filato.

 

Ya ƙara da cewa idan har Najeriya ta tarwatse to ’yan ƙasar, sama da mutum miliyan 50 za su fantsama su tsallaka Turai.

 

Don haka ya ce zai fi zama alheri ga duniya idan Najeriya ta ɗore a matsayin ƙasa guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Nijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso,...

BUA, Ya Raba Ma Ma’aikatansa Kyautar Naira Biliyan 30 a Bikin Ƙarshen Shekara

Shugaban Rukunin Kamfanonin BUA, Alhaji Abdul-Samad Isyaku Rabi’u, ya bai wa dukkan ma’aikatan kamfaninsa kyautar Naira biliyan 30 a matsayin tallafi bisa jajircewarsu a aikin...

Most Popular