HomeSashen Hausa'Yanbindiga sun kai hari a ƙauyuka 16, sun yi ajalin mutum 5,...

‘Yanbindiga sun kai hari a ƙauyuka 16, sun yi ajalin mutum 5, tare da yin garkuwa da wasu da dama a jihar Zamfara.

-

‘Yanbindigar da suka kai hari a ƙalla garuruwa 16 tsakanin Asabar da Lahadi, a ƙaramar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara, sun yi ajalin mutane 5 tare da yin garkuwa da Mata da dama.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, a ranar Asabar, ‘yanbindigar sun yi awon gaba da mutane 8 ciki har da Dan Isa, Kyatawa, Tudu, Gidan Haruna, da sauransu, inda suka kashe mutum 1 a Gidan Haruna kuma suka sace mata 8.

A ranar Lahadi kuma, sun sake dawowa Kwalau inda suka kashe mutum 4, Abubakar, Murtala, Aminu da Bello tare da raunata wani Ashafa, wanda aka kai asibitin Kaura Namoda.

Rahotan jaridar Daily Trust, ya ce ‘yan sa-kai sun yi musayar wuta da ‘yanbindigar a daren Asabar, lamarin da ya sa suka ja da baya.

Sai dai, da safe sun dawo cikin shiri, inda suka kai farmaki wajen taron ‘yan sa-kai, inda suka kashe 4, suka raunata 1, tare da sace Mata da kwashe kayan Abinci da na gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular