HomeSashen HausaKotun Tarayya Ta Yanke Wa Jagoran Ansaru Hukuncin Shekaru 15 a Gidan...

Kotun Tarayya Ta Yanke Wa Jagoran Ansaru Hukuncin Shekaru 15 a Gidan Gyaran Hali

-

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke ma wani jagoran ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, mai suna Mahmud Muhammad Usman (wanda aka fi sani da Abu Bara’a/Abbas/Mukhtar), hukuncin shekaru 15 a gidan gyaran hali bayan ya amsa laifinsa kan tuhumar haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa Usman ya amsa laifin hakar ma’adinai ba tare da izini ba, inda kuɗaɗen da ake samu daga wannan aiki ake zargin yana amfani da su wajen saya makamai domin gudanar da ayyukan ta’addanci.

Abu Bara a da wani ɗan kungiyar, Abubakar Abba (wanda aka fi sani da Isah Adam/Mahmud Al-Nigeri), an gurfanar da su ne bisa zarge-zargen laifuka 32 da suka haɗa da ta’addanci, samar da kudi don ta’addanci da kuma amfani da makamai. Duk da haka, Abba ya ƙi amsa dukkanin tuhumar da ake masa, kuma shari’ar tasa za a ci gaba da saurran ta.

Kotun ta ba da umarnin cewa waɗanda ake tuhuma su ci gaba da zama a hannun Hukumar Tsaro ta Jiha (DSS) yayin da ake cigaba da shari’ar. An dai ɗage sauraron shari’ar sauran tuhume-tuhumen har zuwa 21 ga watan Oktoba, 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Abinda Ya Faru Da Ni Ya Zame Min Alkhairi– Malam Bala Dorayi

Malam Bala Dorayi, wanda aka fi sani da Sarkin Yakin Karyar Ƙasar Hausa, ya bayyana cewa abin da ya faru da shi a baya kaddara...

‎Kim Jong Un Ya Zaɓi Ƴarsa Mai Shekara 13 a Matsayin Wadda Za Ta Gaje Shi ‎

Rahotanni daga National Intelligence Service (NIS) sun bayyana cewa shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un, ya zaɓi ƴarsa mai shekara 13, Kim Ju Ae,...

Most Popular