HomeSashen HausaKotun Tarayya Ta Yanke Wa Jagoran Ansaru Hukuncin Shekaru 15 a Gidan...

Kotun Tarayya Ta Yanke Wa Jagoran Ansaru Hukuncin Shekaru 15 a Gidan Gyaran Hali

-

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke ma wani jagoran ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, mai suna Mahmud Muhammad Usman (wanda aka fi sani da Abu Bara’a/Abbas/Mukhtar), hukuncin shekaru 15 a gidan gyaran hali bayan ya amsa laifinsa kan tuhumar haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa Usman ya amsa laifin hakar ma’adinai ba tare da izini ba, inda kuɗaɗen da ake samu daga wannan aiki ake zargin yana amfani da su wajen saya makamai domin gudanar da ayyukan ta’addanci.

Abu Bara a da wani ɗan kungiyar, Abubakar Abba (wanda aka fi sani da Isah Adam/Mahmud Al-Nigeri), an gurfanar da su ne bisa zarge-zargen laifuka 32 da suka haɗa da ta’addanci, samar da kudi don ta’addanci da kuma amfani da makamai. Duk da haka, Abba ya ƙi amsa dukkanin tuhumar da ake masa, kuma shari’ar tasa za a ci gaba da saurran ta.

Kotun ta ba da umarnin cewa waɗanda ake tuhuma su ci gaba da zama a hannun Hukumar Tsaro ta Jiha (DSS) yayin da ake cigaba da shari’ar. An dai ɗage sauraron shari’ar sauran tuhume-tuhumen har zuwa 21 ga watan Oktoba, 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular