HomeSashen HausaKotun Tarayya Ta Yanke Wa Jagoran Ansaru Hukuncin Shekaru 15 a Gidan...

Kotun Tarayya Ta Yanke Wa Jagoran Ansaru Hukuncin Shekaru 15 a Gidan Gyaran Hali

-

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke ma wani jagoran ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, mai suna Mahmud Muhammad Usman (wanda aka fi sani da Abu Bara’a/Abbas/Mukhtar), hukuncin shekaru 15 a gidan gyaran hali bayan ya amsa laifinsa kan tuhumar haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa Usman ya amsa laifin hakar ma’adinai ba tare da izini ba, inda kuɗaɗen da ake samu daga wannan aiki ake zargin yana amfani da su wajen saya makamai domin gudanar da ayyukan ta’addanci.

Abu Bara a da wani ɗan kungiyar, Abubakar Abba (wanda aka fi sani da Isah Adam/Mahmud Al-Nigeri), an gurfanar da su ne bisa zarge-zargen laifuka 32 da suka haɗa da ta’addanci, samar da kudi don ta’addanci da kuma amfani da makamai. Duk da haka, Abba ya ƙi amsa dukkanin tuhumar da ake masa, kuma shari’ar tasa za a ci gaba da saurran ta.

Kotun ta ba da umarnin cewa waɗanda ake tuhuma su ci gaba da zama a hannun Hukumar Tsaro ta Jiha (DSS) yayin da ake cigaba da shari’ar. An dai ɗage sauraron shari’ar sauran tuhume-tuhumen har zuwa 21 ga watan Oktoba, 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular