HomeSashen HausaMa'aikatar Shari'a Ta Katsina Ta Naɗa Mace Ta Farko A Matsayin Babbar...

Ma’aikatar Shari’a Ta Katsina Ta Naɗa Mace Ta Farko A Matsayin Babbar Magatakarda

-

Ma’aikatar Shari’a ta jihar Katsina ta naɗa Basira Umar a matsayin mace ta farko da za ta rike mukamin Babbar Magatakarda ta Babbar Kotun Katsina tun bayan kafa jihar a 1987.

 

A rahoton Daily Nigerian, wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Musa Usman, Daraktan Hulda da Jama’a na Babbar Kotun jihar, ya fitar ga manema labarai a Katsina a ranar Asabar.

 

A cewarsa, wannan naɗin ya biyo bayan ritayar Malam Mustapha Hassan-Rumah daga aikin gwamnati.

 

Ya bayyana cewa Babban Magatakarda shi ne babban jami’in kula da dukiyar kotu, wanda ke da alhakin tsarawa da gudanar da kasafin kuɗi da sauran harkokin kuɗi.

 

“Haka kuma Babban Magatakarda shi ne shugaban gudanarwa na ma’aikatar shari’a, wanda ke jagorantar harkokin yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Abinda Ya Faru Da Ni Ya Zame Min Alkhairi– Malam Bala Dorayi

Malam Bala Dorayi, wanda aka fi sani da Sarkin Yakin Karyar Ƙasar Hausa, ya bayyana cewa abin da ya faru da shi a baya kaddara...

‎Kim Jong Un Ya Zaɓi Ƴarsa Mai Shekara 13 a Matsayin Wadda Za Ta Gaje Shi ‎

Rahotanni daga National Intelligence Service (NIS) sun bayyana cewa shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un, ya zaɓi ƴarsa mai shekara 13, Kim Ju Ae,...

Most Popular