HomeSashen HausaAn Fara Binciken Tsohon Gwamna Daga Kudanci Kan Zargin Kitsa Juyin Mulki...

An Fara Binciken Tsohon Gwamna Daga Kudanci Kan Zargin Kitsa Juyin Mulki A Najeriya

-

Rahotanni sun bayyana cewa ana binciken wani tsohon gwamna daga ɗaya daga cikin jihohin kudancin Najeriya bisa zargin alaƙa da wasu jami’an soji 16 da aka kama bisa zargin shirya juyin mulki.

 

Majiyoyi sun tabbatar wa da jaridar Daily Trust cewa tsohon gwamnan na iya zama ɗaya daga cikin masu tallafawa shirin da aka ce an tsara aiwatar da shi a ranar 25 ga Oktoba.

 

An ce jami’an da ake tsare da su, ciki har da Brigadier Janar da Kanal, suna aiki a Ofishin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa.

 

Hukumar leken asiri ta tsaro (DIA) ce ke jagorantar binciken, tare da wakilai daga rundunonin soji uku. Majiyoyi sun bayyana cewa tsohon gwamnan yana da tarihi a harkar man fetur da iskar gas, kuma ana iya gayyatarsa idan aka tabbatar da hujjar haɗin kai tsakaninsa da jami’an da ake tsare da su.

 

Sai dai Hedkwatar Tsaron Ƙasa (DHQ) ta karyata labarin cewa akwai yunƙurin juyin mulki, tana mai cewa jami’an da aka kama ana bincikensu ne kan rashin ladabi da karya ƙa’idar aiki, ba wani shirin kifar da gwamnati ba.

 

Shelkwatar tsaron ta jaddada cewa rundunar sojojin Najeriya tana nan daram wajen biyayya ga kundin tsarin mulki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tana kuma roƙon jama’a da su ƙaurace wa yada jita-jita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular