HomeSashen HausaBudurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren...

Budurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren Dole

-

Wata matashiya ta kashe kanta a karamar hukumar Gubio ta jihar Borno, bayan mahaifinta ya tilasta mata aure da ɗaya daga cikin abokansa.

 

Shafin jaridar Zagazola Makama ya rawaito cewa lamarin ya faru ne da yammacin jiya Lahadi da misalin ƙarfe 6:20, inda majiyoyi suka bayyana cewa marigayiyar ta sha matsin lamba daga iyayenta don ta amince da auren da aka shirya mata, duk da cewa tana ƙaunar wani daban.

 

Wani mai sa ido kan kare haƙƙin yara a yankin, Bukar Fantami Gubio, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa damuwa da matsin lambar da ta fuskanta ne suka sa ta ɗauki ranta.

 

Ya yi kira ga hukumomin kare haƙƙin ɗan adam da jami’an tsaro da su gudanar da bincike tare da ɗaukar matakin hana irin wannan auren dole a nan gaba.

 

Rundunar ‘yan sanda da gwamnatin jihar Borno ba su fitar da wata sanarwa ta hukuma kan lamarin ba har zuwa lokacin da ake kammala wannan rahoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular