HomeSashen HausaSojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen Shugaban ’Yan Bindiga, Kallamu, A Jihar Sokoto

Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen Shugaban ’Yan Bindiga, Kallamu, A Jihar Sokoto

-

Sojojin Rundunar 8 Division ta Najeriya a Sokoto sun samu gagarumar nasarar kawar da fitaccen shugaban ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a yankin Sabon Birni, Jihar Sokoto.

 

An kashe Kallamu ne a wani samame na musamman da sojoji suka gudanar tare da hadin gwiwar ’yan sa-kai a yankin Kurawa, da safiyar Litinin.

 

Kallamu, wanda babban na hannun daman shugaban ’yan bindiga Bello Turji ne, ya kasance daya daga cikin wadanda suka addabi al’ummar Sabon Birni da hare-hare, garkuwa da mutane da kuma tada tarzoma a yankin.

 

Rahotonni sun bayyana cewa an kashe shi ne tare da daya daga cikin manyan masu samar wa Turji da kayan aiki da bayanan sirri, a wani artabu da ya faru da safiyar litinin.

 

Rahotanni sun ce Kallamu, wanda asalinsa daga Garin-Idi a Sabon Birni, ya dawo ne cikin yankin bayan tserewa wani farmaki da sojoji suka kai masa a watan Yunin 2025, inda ake zargin ya shige Kogi domin buya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu A Najeriya

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu daga Aminiya, an tabbatar da cewa, tsofaffin ma’aikatan (FRCN) Federal Radio Corporation of Nigeria (FRCN) sun ce...

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina Wata mata mai juna...

Most Popular