Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso, Burkina Faso, ya je aikin leken asiri a boye.
Runudunar ta ce rahoton karya ne kuma ba shi da tushe, tana mai jaddada cewa jirgin na kan hanyarsa ta zuwa Portugal domin gyara, kuma saukar gaggawar da ya yi ta faru ne saboda dalilan tsaro bisa ka’idojin sufurin jiragen sama na duniya.
Bayanai da Jaridar The Nation sun ce wata majiya a hedkwatar tsaron NAF ta ce jirgin yana dauke da dukkan takardun izini, kuma an bi dukkan matakan da doka ta tanada.
