HomeSashen HausaNijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

Nijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

-

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso, Burkina Faso, ya je aikin leken asiri a boye.

 

Runudunar ta ce rahoton karya ne kuma ba shi da tushe, tana mai jaddada cewa jirgin na kan hanyarsa ta zuwa Portugal domin gyara, kuma saukar gaggawar da ya yi ta faru ne saboda dalilan tsaro bisa ka’idojin sufurin jiragen sama na duniya.

 

Bayanai da Jaridar The Nation sun ce wata majiya a hedkwatar tsaron NAF ta ce jirgin yana dauke da dukkan takardun izini, kuma an bi dukkan matakan da doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Duniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa a Najeriya, Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taɓa bari Najeriya ta ruguje a hannunta ba, komai rintsi.   Kamar yadda...

BUA, Ya Raba Ma Ma’aikatansa Kyautar Naira Biliyan 30 a Bikin Ƙarshen Shekara

Shugaban Rukunin Kamfanonin BUA, Alhaji Abdul-Samad Isyaku Rabi’u, ya bai wa dukkan ma’aikatan kamfaninsa kyautar Naira biliyan 30 a matsayin tallafi bisa jajircewarsu a aikin...

Most Popular