HomeSashen HausaOdua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan...

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle

-

Sun ce, zargin alaƙa da ‘yan bindiga barazana ce ga tsaron Najeriya.

 

Ƙungiyar Odua People’s Assembly (OPA) ta nuna damuwa matuƙa kan zargin da ake yi wa Ministan Tsaron Ƙasa (State), Bello Matawalle, dangane da alaƙa da ‘yan bindiga. Ƙungiyar ta ce zargin yana da hatsari ga tsaron ƙasa da amincewar jama’a.

 

OPA ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da sanya gaskiya kuma ba tare da son kai ba, domin fayyace gaskiyar lamarin. Ta ce rashin daukar mataki zai ƙara raunana amincewar jama’a da hukumomin gwamnati, musamman a lokacin da Najeriya ke fama da matsanancin matsalar tsaro.

 

Ƙungiyar ta ce bayyanar wani bidiyo da ke nuna Bello Turji, shugaban ‘yan bindiga, yana kare Matawalle abin tayar da hankali ne, domin yana nuna yiyuwar haɗin kai tsakanin jami’an gwamnati da masu laifi.

 

OPA ta bayyana cewa duk wata alaƙa, kai tsaye ko a kaikaice, tsakanin jami’an gwamnati da ‘yan bindiga cin amanar ‘yan Najeriya ne, musamman waɗanda suka sha wahala sakamakon rashin tsaro.

 

A matsayin mataki na dawo da amincewar jama’a, OPA ta buƙaci a sauke Matawalle daga muƙaminsa nan take, tare da kafa cikakken tsari na bincike mai zaman kansa. Ta kuma gargadi cewa rashin daukar mataki mai tsauri zai ƙarfafa ‘yan bindiga tare da ƙara ta’azzara rashin tsaro.

 

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu faɗakarwa, su kuma riƙa kira ga alhakin shugabanni, tana jaddada cewa yaƙi da ‘yan bindiga ya zama na bai ɗaya, ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba.

 

Sa Hannun;

Sunday Daniel

Mai magana da yawun Odua People’s Assembly

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular