HomeLabarai‎Gwamnan Gombe Ya Kori Wasu hadimansa Huɗu Kan Zargin Cin Zarafin Kansila

‎Gwamnan Gombe Ya Kori Wasu hadimansa Huɗu Kan Zargin Cin Zarafin Kansila

-

Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya kori wasu hadimansa huɗu daga aiki nan take, bayan an same su da laifin cin zarafin wani kansila mai ci, Abdulrahman Abubakar Sharif, mai wakiltar yankin Shamaki a ƙaramar hukumar Gombe.

‎Matakin ya biyo bayan rahoton kwamitin bincike da bayanan jami’an tsaro, kamar yadda Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya bayyana.

‎Waɗanda aka kora sun haɗa da Adamu Abdullahi Danko, Garba Mohammed Mai Rago, Rabiu Suleman Abubakar da Alhaji Ibrahim Baban Kaya, dukkaninsu Mataimaka ne na Musamman (SAS II) a fannoni daban-daban.

‎Gwamnatin jihar ta umurce su da su miƙa dukkan kayayyakin gwamnati da ke hannunsu nan take.

‎A sanarwar da Babban Daraktan Yaɗa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnatin ta jaddada cewa ba za ta lamunci cin zarafi ba, tare da ci gaba da kare doka, adalci da zaman lafiya a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Arrest Suspected Kidnapper, Bandit Informant in Matazu

The Katsina State Police Command has arrested a 45-year-old man, identified as Surajo Isyaku, over alleged involvement in kidnapping, cattle rustling and providing information to...

Dangote Refinery Reduces Aviation Fuel Price by N100 Per Litre

Dangote Refinery has announced a reduction in the price of Jet A1 aviation fuel from N1,750 to N1,650 per litre, in a move aimed at...

Most Popular