HomeSashen Hausa'Yansanda Sun Kama 'Yanbindigar Da Bidiyonsu Ya Yaɗu Su Na Nuna Makamai...

‘Yansanda Sun Kama ‘Yanbindigar Da Bidiyonsu Ya Yaɗu Su Na Nuna Makamai da Kuɗaɗe a Kwara

-

Rundunar ƴansandan Nijeriya ta kama wasu mutane biyu da ake zargi ‘yan fashin daji ne da garkuwa da mutane a jihohin Katsina, Zamfara, Neja da Kwara.

 

An kama su ne a ranar 19 ga Disamba a yankin Komen–Masallaci da ke karamar hukumar Kaiama ta jihar Kwara.

 

Daya daga cikin wadanda aka kama, Abubakar Usman (Siddi), shi ne wanda aka gani a bidiyon da ya yadu yana nuna makamai da kudi, yayin da na biyun shi ne Shehu Mohammadu (Gide).

 

Jami’an tsaro sun kwato babur Honda Ace 125, kudi N500,000 da bindigar AK-47 tare da harsashi 20.

 

Ƴansanda sun ce bincike ya nuna cewa su mambobi ne na wata kungiyar ‘yan fashin daji da ke addabar jihohi da dama, kuma suna hada-hadar samar da makamai.

 

Rundunar ta ce wadanda ake zargin suna bada hadin kai ga masu bincike, tare da bukatar jama’a su rika bayar da sahihan bayanai domin taimakawa ayyukan tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular