HomeSashen HausaAfenifere Ta Goyi Bayan Harin Da Amurka Ta Kai a Sokoto

Afenifere Ta Goyi Bayan Harin Da Amurka Ta Kai a Sokoto

-

Kungiyar Afenifere, wadda ke wakiltar al’ummar Yarbawa a fannin siyasa da zamantakewa, ta bayyana goyon bayanta ga hare-haren jiragen yakin Amurka da aka kai kan sansanonin kungiyar ta’addanci ta ISIS a jihar Sokoto.

 

Kungiyar ta yaba wa gwamnatin tarayya bisa abin da ta bayyana a matsayin hare-haren da suka kasance masu muhimmanci kuma a kan lokaci, duba da halin rashin tsaro da ke kara ta’azzara a sassan kasar nan.

 

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta tabbatar da cewa an gudanar da harin ne ta hanyar hadin gwiwa tsakanin Najeriya da Amurka, domin kai wa sansanonin ‘yan ta’addan ISIS da ke jihar Sokoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Majalisar Wakilai Ta Umarci A Yi Gyare-gyare a Kundin Sabbin Dokokin Haraji Bayan Samun Kura-kurai

Majalisar Wakilai ta bayar da umarnin sake duba sabbin dokokin gyaran haraji da aka amince da su kwanan nan, biyo bayan zargin bambance-bambance tsakanin dokokin...

Harin Da Amurka Ta Kai ‘Yan ta’adda Ne Kaɗai Ya Shafa– Inji Gwamnatin Sokoto

Gwamnatin Jihar Sokoto ta tabbatar da cewa harin sama na haɗin gwiwar sojojin Najeriya da Amurka ya kai hari kan sansanonin ’yan ta’adda a ƙaramar...

Most Popular