HomeSashen Hausa‎Majalisar Wakilai Ta Umarci A Yi Gyare-gyare a Kundin Sabbin Dokokin Haraji...

‎Majalisar Wakilai Ta Umarci A Yi Gyare-gyare a Kundin Sabbin Dokokin Haraji Bayan Samun Kura-kurai

-

Majalisar Wakilai ta bayar da umarnin sake duba sabbin dokokin gyaran haraji da aka amince da su kwanan nan, biyo bayan zargin bambance-bambance tsakanin dokokin da majalisar ƙasa ta amince da su da kuma waɗanda aka wallafa bayan shugaban ƙasa ya sanya hannu.

‎Kakakin Majalisar, Akin Rotimi, ya ce matakin ya zama dole domin kare mutuncin majalisa, tabbatar da bin ƙa’idoji, da dawo da amincewar jama’a ga tsarin yin dokoki.

‎Ya bayyana cewa duk wani bambanci tsakanin kudurin doka da aka amince da shi da waɗanda aka wallafa na tauye dimokuraɗiyya da manufar dokoki.

‎Majalisar ta jaddada cewa dokokin haraji, saboda tasirinsu ga tattalin arziƙi, dole ne su kasance a bayyane, daidai, kuma bisa tsarin kundin mulki.

‎Ta kuma tabbatar da cewa za ta yi aiki da hukumomin zartarwa domin gyara matsalar tare da hana sake faruwarta, tana mai jaddada goyon baya ga gyare-gyaren da ke ƙarfafa tattalin arziƙi matuƙar an bi ka’idojin doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular