HomeLabarai‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam'iyyar...

‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam’iyyar NNPP

-

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya amince da bai wa ’ya’yan ’yan Majalisar Jiha biyu da suka rasu, damar tsayawa takara, domin neman cike guraben kujerun iyayensu a Majalisar Dokokin Jihar ta Kano.

‎Matakin wanda ya shafi kujerun wakilcin Ungogo da Birnin Kano, inda ’ya’yan kowane daya daga cikin ’yan majalisar za su fafata a zaben cike gurbin kujerun karkashin tutar jam’iyyar NNPP.

‎Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun bayyana cewa wannan mataki na daga cikin kokarin NNPP na tabbatar da ci gaba da wakilci da kuma girmama gudunmawar da ’yan majalisar suka bayar wajen hidimar al’ummar yankunansu a lokacin da suke raye.

‎Ana sa ran wannan mataki zai jawo ra’ayoyi mabanbanta a fagen siyasar Jihar Kano, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zabukan cike gurbin kujerun da ke tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

NPFL Orders Barau FC vs Katsina United Clash Behind Closed Doors

The Nigeria Premier Football League (NPFL) has approved a request by Barau FC for their match against Katsina United FC to be played without fans...

Nigeria Edge Iran 2–1 in International Friendly

The Nigeria national football team, the Super Eagles, defeated Iran 2–1 in a friendly match played on Friday. The match took place at the Mardan Sport...

Most Popular