HomeLabarai‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam'iyyar...

‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam’iyyar NNPP

-

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya amince da bai wa ’ya’yan ’yan Majalisar Jiha biyu da suka rasu, damar tsayawa takara, domin neman cike guraben kujerun iyayensu a Majalisar Dokokin Jihar ta Kano.

‎Matakin wanda ya shafi kujerun wakilcin Ungogo da Birnin Kano, inda ’ya’yan kowane daya daga cikin ’yan majalisar za su fafata a zaben cike gurbin kujerun karkashin tutar jam’iyyar NNPP.

‎Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun bayyana cewa wannan mataki na daga cikin kokarin NNPP na tabbatar da ci gaba da wakilci da kuma girmama gudunmawar da ’yan majalisar suka bayar wajen hidimar al’ummar yankunansu a lokacin da suke raye.

‎Ana sa ran wannan mataki zai jawo ra’ayoyi mabanbanta a fagen siyasar Jihar Kano, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zabukan cike gurbin kujerun da ke tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Foil Kidnap Attempt, Rescue 18-Year-Old Girl in Danmusa LG

The Katsina State Police Command has foiled a kidnapping attempt and rescued an 18-year-old girl in Danmusa Local Government Area following a swift response by...

Harin Sojin Sama a Zamfara Ya Hallaka Sama da Mutane 100

A cikin wata sanarwa da rundunar Operation Fansan Yamma ta fitar, ta ce an kai harin ne bayan samun sahihan bayanan sirri da suka nuna...

Most Popular