HomeSashen Hausa‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam'iyyar...

‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam’iyyar NNPP

-

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya amince da bai wa ’ya’yan ’yan Majalisar Jiha biyu da suka rasu, damar tsayawa takara, domin neman cike guraben kujerun iyayensu a Majalisar Dokokin Jihar ta Kano.

‎Matakin wanda ya shafi kujerun wakilcin Ungogo da Birnin Kano, inda ’ya’yan kowane daya daga cikin ’yan majalisar za su fafata a zaben cike gurbin kujerun karkashin tutar jam’iyyar NNPP.

‎Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun bayyana cewa wannan mataki na daga cikin kokarin NNPP na tabbatar da ci gaba da wakilci da kuma girmama gudunmawar da ’yan majalisar suka bayar wajen hidimar al’ummar yankunansu a lokacin da suke raye.

‎Ana sa ran wannan mataki zai jawo ra’ayoyi mabanbanta a fagen siyasar Jihar Kano, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zabukan cike gurbin kujerun da ke tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular