HomeSashen Hausa‎Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar da Hukuncin Kisa ga Abdulmalik Tanko

‎Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar da Hukuncin Kisa ga Abdulmalik Tanko

-

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin kisa da aka yanke wa Abdulmalik Tanko, wanda aka samu da laifin garkuwa da kuma kashe Hanifa, yarinya ƴar shekara takwas, Kotun ta yanke wannan hukunci ne bayan duba ƙarar da aka shigar, inda ta ce hujjojin da aka gabatar sun isa su tabbatar da laifukan da aka tuhumi wanda ake ƙara.

Mai shari’a A.R. Muhammad, wanda ya jagoranci zaman kotun, ya bayyana cewa hukuncin da kotun ƙasa ta yanke ya yi dai dai da tanadin doka, kuma babu wani kuskure a shari’ar da zai sa a soke ko a rage hukuncin, Ya ƙara da cewa an bi dukkan matakan shari’a yadda ya kamata tun daga matakin bincike har zuwa yanke hukunci.

Kotun ta kuma ja hankalin gwamnati da ta gaggauta aiwatar da hukuncin kisa, domin tabbatar da adalci ga iyalan wadda abin ya shafa, hana aikata laifuka makamantan haka a nan gaba, da kuma kare al’umma daga miyagun laifuka.

Hukuncin ya jawo martani daga al’umma, inda da dama ke ganin cewa matakin da kotu ta ɗauka zai zama darasi ga masu aikata laifukan garkuwa da kashe kashe, musamman waɗanda ke shafar yara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

DA DUMI-DUMI: Bam Ya Tashi A Babbar Asibitin Jihar Kebbi

Rundunar ‘yansanda a jihar Kebbi ta tabbatar da afkuwar fashewar bam da sanyin safiyar Talata a babban asibitin Bagudo, da ke karamar hukumar Bagudo ta...

Kwamandan NSCDC Katsina, Ya Nemi Goyon Bayan Masarautar Katsina Kan Inganta Tsoron Al’umma

Kwamandan Rundunar NSCDC a Jihar Katsina, Commandant AD Moriki, ya kai ziyara bangirma a Fadar Sarkin Katsina, inda aka sanya ma sa albarka da shawarwari...

Most Popular