HomeSashen Hausa‎Jirgin Marar Matuƙi Ya Faɗo a Dajin Kontagora, Jihar Neja

‎Jirgin Marar Matuƙi Ya Faɗo a Dajin Kontagora, Jihar Neja

-

Wani jirgin marar matuƙi (drone) ya faɗo a wani daji da ke kusa da garin Kontagora, a Jihar Neja, da yammacin yau Juma’a, kamar yadda majiyoyi suka tabbatar.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne ba tare da jikkata kowa ba, yayin da har yanzu ba a tabbatar da dalilin faɗuwar jirgin ba, Wasu mazauna yankin sun ce sun ji ƙara mai ƙarfi kafin daga bisani suka ga jirgin ya faɗo a cikin dajin.

‎Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, jami’an tsaro basu fitar da wata sanarwa a hukumance ba dangane da mallakar jirgin ko manufar tashi da aka yi da shi.

‎Sai dai ana sa ran jami’an tsaro za su fara bincike domin gano musabbabin faɗuwar jirgin da kuma ko akwai wata barazana ga tsaron al’umma.

Hukumomi sun shawarci al’umma da su nisanci yankin da lamarin yafaru, tare da bai wa jami’an tsaro damar gudanar da aikinsu cikin kwanciyar hankali.

Za mu cigaba da bibiyar lamarin tare da kawo muku ƙarin bayani da zarar an samu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular