HomeLabaraiDikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

Dikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

-

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da naɗin sabbin manyan sakatarorin jihar.

 

Gwamnan ya ce an gudanar da naɗin bi sa cancanta da sabbin manyan sakatarorin da aka naɗa suka nuna ta hanyar cin jarabawar da Cibiyar Ma’aikata ta Najeriya ta gudanar a madadin gwamnatin jihar Katsina.

 

Gwamnan wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan jihar Mallam Falalu Bawale, ya buƙaci waɗanda aka naɗan da su yi aiki da ƙwarewa tare da nuna ƙwazo.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, sabbin manyan sakatarorin sun haɗa da Tukur Hassan Dan Ali, Junaidu Muntari da Yahaya Abdullahi.

 

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai na shugaban ma’aikatan jihar Abubakar Yaro Bindawa ya fitar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Atletico Knock Out Barcelona to Secure First Semifinal Spot in Eight Years

Atlético Madrid reached the semifinals for the first time since 2017 after knocking out FC Barcelona. Barcelona started the match strongly, with Lamine Yamal and Ferran...

FG Denies ADC Use of Eagle Square for Abuja Convention

The African Democratic Congress (ADC) has said it was denied access to both Eagle Square and the Moshood Abiola National Stadium for its planned national...

Most Popular