HomeSashen HausaJaruma Rahama Sadau, Ta Shirya Bikin Fina-finan Arewacin Najeriya

Jaruma Rahama Sadau, Ta Shirya Bikin Fina-finan Arewacin Najeriya

-

Fitacciyar jaruma a masana’antar Kannywood da Nollywood, Rahama Sadau, ta shirya bikin ɗaga darajar fina-finan Arewacin Najeriya.

 

Jarumar ta ce ta shirya bikin ne domin tallata fina-finan Arewacin Nijeriya domin ɗaga martabar fina-finan da zummar samun karɓuwa a ƙetare.

 

Rahama Sadau ta bayyana hakan ne a yayin jawabin da ta gabatar a wajen bikin fina-finan da aka gudanar a dandalin Murtala Square da ke Jihar Kaduna.

 

Manyan jaruman Kannywood da suka yi fice, ciki har da Ali Jiya, Umar M. Shareef, Abdul D One da sauran fitattun ’yan fim, sun halarci taron waɗanda suka fito domin nuna goyon baya ga jarumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Malami Ya Zargi DSS da Tauye Masa ’Yancin Kare Kansa a Kotu

‎Tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya zargi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) da daukar matakan hana shi cikakken...

Kamfanin Shell Ya Yi Alƙawarin Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Najeriya Bayan Dala Biliyan 7 Da Aka Kashe– NNPCL GCEO

Shugaban Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL), Mista Bashir Bayo Ojulari, ya bayyana cewa Kamfanin Shell Petroleum Development Company ya kuduri aniyar neman...

Most Popular