Monday, June 29, 2026
HomeLabaraiJaruma Rahama Sadau, Ta Shirya Bikin Fina-finan Arewacin Najeriya

Jaruma Rahama Sadau, Ta Shirya Bikin Fina-finan Arewacin Najeriya

Fitacciyar jaruma a masana’antar Kannywood da Nollywood, Rahama Sadau, ta shirya bikin ɗaga darajar fina-finan Arewacin Najeriya.

 

Jarumar ta ce ta shirya bikin ne domin tallata fina-finan Arewacin Nijeriya domin ɗaga martabar fina-finan da zummar samun karɓuwa a ƙetare.

 

Rahama Sadau ta bayyana hakan ne a yayin jawabin da ta gabatar a wajen bikin fina-finan da aka gudanar a dandalin Murtala Square da ke Jihar Kaduna.

 

Manyan jaruman Kannywood da suka yi fice, ciki har da Ali Jiya, Umar M. Shareef, Abdul D One da sauran fitattun ’yan fim, sun halarci taron waɗanda suka fito domin nuna goyon baya ga jarumar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments