HomeSashen Hausa‎Malami Ya Zargi DSS da Tauye Masa ’Yancin Kare Kansa a Kotu

‎Malami Ya Zargi DSS da Tauye Masa ’Yancin Kare Kansa a Kotu

-

‎Tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya zargi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) da daukar matakan hana shi cikakken ’yancinsa na shari’a da kare kansa yadda doka ta tanada.

‎A cikin wata sanarwa da Mai Taimaka Masa kan Harkokin Yaɗa Labarai, Mohammed Bello Doka, ya sanya wa hannu, Malami ya ce DSS na ci gaba da hana lauyoyinsa damar ganinsa, lamarin da ya hana shi tuntuba, ba da umarni, da kuma shirya takardun shari’a yadda ya dace.

‎Malami ya bayyana hakan a matsayin tauye hakkokin ɗan Adam, yana mai cewa irin waɗannan matakai sun sabawa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin Najeriya.

‎“Abin da ke faruwa ya nuna wani salo da ake fara kama mutum kafin bincike, sannan a fara neman hujjoji bayan tsare shi, wanda hakan ya saɓa doka da kuma ’yancin da kundin tsarin mulki ya tanada,” in ji sanarwar.

‎Ya ƙara da cewa abin damuwa ne matuƙa ganin yadda DSS ke aiwatar da abin da ya kira tsarewa, sannan neman hujjoji daga baya, yana mai jaddada cewa hakan barazana ce ga bin doka da oda ta ƙasa.

‎Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, DSS ba ta fitar da wata sanarwar martani kan zargin da tsohon Ministan ya yi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular